I M S Online Tv

I M S Online Tv Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from I M S Online Tv, GRA Rima Roundabout Opposite Ambursa Electronics Birnin Kebbi, Birnin-Kebbi.

Tashar I M S ONLINE TV Wato Information mangment Service tasha c Wadda k Kokarin Kawo mku Rahottanni Labarun Ksa Gmi dn Ktare Wdnda ska Shafi Siyasa D Raywar Al-umma t yau d Kullum Kai Tsye a Babbn Ofishin t dke GRA Joda Street Ksa g Corespondnt Charpels

Gwamnatin Jahar Neja tayi Alkawarin Tabbatar da Adalci a Zaben Fidda Gwani na Jam'iyyar APC Gwamnan Jihar Neja, Mohammed...
14/05/2026

Gwamnatin Jahar Neja tayi Alkawarin Tabbatar da Adalci a Zaben Fidda Gwani na Jam'iyyar APC

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya bai wa dukkan masu neman takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC tabbacin gudanar da zaɓen fidda gwani na kai tsaye cikin adalci, gaskiya da kuma nuna cikakken tsari a wuraren da ba a cimma matsayar maslaha ba.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Bologi Ibrahim, ya sanya wa hannu, inda ya ce gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron dabaru da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar tare da dukkan masu neman takara na APC a dakin taro na Hauwa Wali Multipurpose Hall da ke gidan gwamnatin jihar a Minna.

Gwamna Bago ya bayyana cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa da masu neman takara domin samar da maslaha da rage rikice-rikice tare da ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar.
Yayin da ya jaddada cewa jadawalin gudanar da zaɓen fidda gwani bai sauya ba, gwamnan ya bayyana cewa za a gudanar da zaɓen ne a hedikwatar kowace mazaɓa daga cikin mazaɓun jihar baki ɗaya.

Ya kuma gargadi masu neman takara da su guji kawo ’yan daba domin tayar da tarzoma yayin gudanar da zaɓen, yana mai cewa duk wanda aka k**a da hannu wajen hakan na iya fuskantar hukuncin dakatarwa daga takara. Haka kuma ya ce duk wanda ba ɗan jam’iyya ba da aka samu yana kawo cikas za a ɗauki mataki mai tsauri a kansa.

Gwamnan ya yabawa masu neman takarar da s**a janye daga neman muƙami tare da rungumar tsarin maslaha, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da aiki tare da su tare da saka musu da irin sadaukarwar da s**a yi domin ci gaban jam’iyyar.

Har ila yau, ya gode wa jam’iyyar APC bisa nasarar tantance dukkan masu neman takara ba tare da an samu wanda aka dakatar ba, tare da yaba wa duk wadanda s**a halarci taron.

Da yake nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris, ya yabawa Gwamna Bago bisa irin jagorancin da yake bayarwa a cikin jam’iyyar, wanda ya sa da dama daga cikin masu neman takara s**a janye aniyarsu domin samar da haɗin kai.

Ya bayyana cewa wannan wani lokaci ne mai kyau ga jam’iyyar APC da mambobinta, yana mai nuna kwarin gwiwa cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana ba tare da rikici ba, wanda zai zama abin koyi ga sauran jihohin ƙasar nan.

A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Neja, CP Adamu Abdullahi Elleman, ya bukaci masu neman takara da mambobin jam’iyyar da su gudanar da harkokinsu cikin lumana, tare da tabbatar musu da cewa jami’an tsaro za su samar da cikakken tsaro a dukkan mazaɓu 274 na jihar.

CP Elleman ya kuma bukaci dukkan masu neman takara da su je hedikwatar ’yan sanda a ranar Alhamis domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, wadda ya ce tana da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da zaɓen fidda gwani.

Shugaban APC na shiyyar Arewa ta Tsakiya, Mu’azu Bawa Rijau, da Shugaban APC na jihar, Aminu Musa Bobi, tare da sauran masu ruwa da tsaki da s**a yi jawabi a taron, sun jaddada muhimmancin haɗin kai da gudanar da zaɓen cikin lumana.

Wasu daga cikin masu neman takarar da s**a janye daga takara sun bayyana cewa sun ɗauki matakin ne saboda girmamawa da kuma salon shugabanci na bai wa kowa dama da Gwamna Bago ke nunawa, tare da alƙawarin ci gaba da kasancewa masu biyayya ga jam’iyyar APC.

Tinubu Arrives Kigali Ahead of Africa CEO Forum Economic DiscussionsPresident Bola Ahmed Tinubu has arrived in Kigali, R...
14/05/2026

Tinubu Arrives Kigali Ahead of Africa CEO Forum Economic Discussions

President Bola Ahmed Tinubu has arrived in Kigali, Rwanda, to participate in the 13th edition of the Africa CEO Forum, where African leaders and investors are expected to discuss economic reforms, regional integration and private sector growth across the continent.

The President arrived on Wednesday, May 13, 2026, according to a statement issued by his special adviser on information and strategy, Bayo Onanuga, who said Tinubu was received at Kigali International Airport by Nigerian and Rwandan government officials, including Rwanda’s defence minister, Juvenal Marizamunda. Kigali Africa CEO Forum 2026.

The annual forum, founded in 2012 by Jeune Afrique Media and co-hosted by the International Finance Corporation, has grown into one of Africa’s largest gatherings of business leaders, policymakers and investors focused on economic transformation and cross-border investment opportunities.

This year’s summit is themed “The Scale Imperative: Why Africa Must Embrace Shared Ownership”, with discussions expected to centre on regional cooperation, sustainable development and strengthening African economies amid global economic uncertainties.

President Tinubu is scheduled to deliver a keynote session titled “Holding the Line: Nigeria’s Reform Bet in a Fractured World”, where he is expected to highlight the impact of ongoing economic reforms and Nigeria’s investment outlook.

The president is also expected to hold bilateral meetings with African and international business leaders to explore partnerships capable of boosting trade, infrastructure development and private sector investment in Nigeria and across Africa.

Officials said the visit would further reinforce Nigeria’s commitment to African unity, regional economic cooperation and long-term development driven by the private sector. International Finance Corporation.

Waye ze fada mana wannan kwaron? Muna yawan chinsa. Baya rayuwa a ko ina sai a chikin Abinchin da muke amfani dashi kull...
14/05/2026

Waye ze fada mana wannan kwaron?

Muna yawan chinsa. Baya rayuwa a ko ina sai a chikin Abinchin da muke amfani dashi kullum. Da Kauye da birni duk muna chinsa a abinchi. Wanda ya sani mu hadu a comment section…👇🏻😂

Daga Aminu Garba Birnin Tudu

13/05/2026

"Kaura Wani Gwamna ne da Allah yaba Jahar Kebbi Wanda aka Cema Koda Naka Kaso Wanga"

"Kuma Suna Kallo Kaura Zaiwa Chika Malami Mugun Bugu a Siyasa Chika ko Kidan Kuri'a tai bai Bari Ayi"
👇👇👇

IBTILA'I: Matashi Ɗan jihar Kano ya yanke gaban sa a Libya Wani matashi ɗan asalin jihar Kano da aka baiyana sunan sa da...
13/05/2026

IBTILA'I: Matashi Ɗan jihar Kano ya yanke gaban sa a Libya

Wani matashi ɗan asalin jihar Kano da aka baiyana sunan sa da Sani, ɗan unguwar Tukuntawa da ke ƙaramar hukumar Birni, ya yanke gaban sa a ƙasar Libya, inda ya tafi domin neman kuɗi.

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa matashin ya aikata hakan ne sak**akon laurar ƙwaƙwalwa da ya kamu da ita a can ƙasar ta Libya.

Da ya ke shaidawa wannan jarida labarin da ya faru, kakakin ƙungiyar Northern Nigerian Organization (NNO), ƙungiyar ƴan Arewacin Najeriya mazauna Libiya, Abba Na-Gaida Fagge ya ce matashin ya samu larurar ƙwaƙwalwa yana watannin baya.

A cewar Fagge, kafin ya yanke gaban nasa, sun samu labarin cewa matashin ya tuka motar katafila a kamfanin da ya ke aiki, inda ya rushe wani gini, lamarin da ya sa mahukunta a kamfanin su ka bada umarnin killace shi.

Ya kara da cewa bayan an killace matashin ne sai kuma ba a san ya aka yi ba, sai ji aka yi ya na ihu, inda ya kara da cewa ko da aka zo aka duba sai aka gan shi kace-kace cikin jini.

"Bayan an kira mu, mu na zuwa ya rike ni wando da duk jini. Muna dubawa mu ka ya yanke gaban sa saura kadan ya rage ya fice daga jikin sa. Wannan lamari ya tayar mana da hankali," in ji Fagge.

Ya kara da cewa basu san me ya same.shi har ta kai ga ya samu larurar ƙwaƙwalwa na, sai dai kuma Fagge ya kara da cewa tuni su ka haɗa kuɗi a junansu su ka kai shi asibiti.

"Yanzu haka aiki za a yi masa a asibitin tunda gaban nasa bai karasa gutsirewa ba."

Ya kuma koka da cewa tun farkon fara ciwon nasa s**a sanar da ofishin jakadancin Nijeriya na Libya amma basu dauki wani mataki ba.

Ya kara da cewa yanzu dai matashin ya na asibiti ya na samun kulawar likitoci, inda ya ce sun sanar da ofishin jakadancin Nijeriya don dawo da shi gida Kano.

" Idan kuma hakan bai samu ba, za mu hada kudi-kudi mu dauki nauyin dawowar da a jirgi zuwa gida don a yi masa magani na ciwon ƙwaƙwalwar ta daIBTILA'I: Matashi ɗan jihar Kano ya yanke gaban sa a Libya

Wani matashi ɗan asalin jihar Kano da aka baiyana sunan sa da Sani, ɗan unguwar Tukuntawa da ke ƙaramar hukumar Birni, ya yanke gaban sa a ƙasar Libya, inda ya tafi domin neman kuɗi.

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa matashin ya aikata hakan ne sak**akon laurar ƙwaƙwalwa da ya kamu da ita a can ƙasar ta Libya.

Da ya ke shaidawa wannan jarida labarin da ya faru, kakakin ƙungiyar Northern Nigerian Organization (NNO), ƙungiyar ƴan Arewacin Najeriya mazauna Libiya, Abba Na-Gaida Fagge ya ce matashin ya samu larurar ƙwaƙwalwa yana watannin baya.

A cewar Fagge, kafin ya yanke gaban nasa, sun samu labarin cewa matashin ya tuka motar katafila a kamfanin da ya ke aiki, inda ya rushe wani gini, lamarin da ya sa mahukunta a kamfanin su ka bada umarnin killace shi.

Ya kara da cewa bayan an killace matashin ne sai kuma ba a san ya aka yi ba, sai ji aka yi ya na ihu, inda ya kara da cewa ko da aka zo aka duba sai aka gan shi kace-kace cikin jini.

"Bayan an kira mu, mu na zuwa ya rike ni wando da duk jini. Muna dubawa mu ka ya yanke gaban sa saura kadan ya rage ya fice daga jikin sa. Wannan lamari ya tayar mana da hankali," in ji Fagge.

Ya kara da cewa basu san me ya same.shi har ta kai ga ya samu larurar ƙwaƙwalwa na, sai dai kuma Fagge ya kara da cewa tuni su ka haɗa kuɗi a junansu su ka kai shi asibiti.

"Yanzu haka aiki za a yi masa a asibitin tunda gaban nasa bai karasa gutsirewa ba."

Ya kuma koka da cewa tun farkon fara ciwon nasa s**a sanar da ofishin jakadancin Nijeriya na Libya amma basu dauki wani mataki ba.

Ya kara da cewa yanzu dai matashin ya na asibiti ya na samun kulawar likitoci, inda ya ce sun sanar da ofishin jakadancin Nijeriya don dawo da shi gida Kano.

" Idan kuma hakan bai samu ba, za mu hada kudi-kudi mu dauki nauyin dawowar da a jirgi zuwa gida don a yi masa magani na ciwon ƙwaƙwalwar tasa," in ji Fagge.," in ji Fagge.

12/05/2026

"Muna Rokon Allah ya Kara Taimakawa Gwamnatin Jihar Kebbi, kuma Gwamnan Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu ya Kara Rike Mana Dr. Bello Sarki Zabarmawan Koko-Besse Amana" A Cewar Yan Kungiyar Sorohinka dake Karamar Hukumar Mulkin Bagudu

12/05/2026

A Kokarin Shi na Kara Bada Gudummawa ga Gwamna Dr Nasir Idris Dr. Bello Bezan Sarkin Zabarmawan Koko-Besse ya Gudanar da Tallafin Rabon Mashuna a Karamar Hukumar Mulkin Bagudu

CHAIRMAN OF KEBBI PILGRIMS WELFARE AGENCY JOINS INTERNATIONAL FLIGHT CREW IN SYMBOLIC SHOW OF UNITYThe Chairman of the K...
07/05/2026

CHAIRMAN OF KEBBI PILGRIMS WELFARE AGENCY JOINS INTERNATIONAL FLIGHT CREW IN SYMBOLIC SHOW OF UNITY

The Chairman of the Kebbi State Pilgrims Welfare Agency, Alhaji Faruku Aliyu Enabo, Jagaban Gwandu, was at the center of a memorable group photograph alongside members of the international flight crew responsible for the transportation of Kebbi State pilgrims to the Kingdom of Saudi Arabia for the Hajj exercise.

The photograph, taken inside the aircraft shortly before departure, captured a moment of friendship, professionalism, and solidarity as the chairman and members of the crew proudly raised two fingers a symbolic gesture widely recognised by supporters as an expression of support for the Kebbi State Government’s second-term continuity agenda.

Alhaji Faruku Aliyu Enabo, popularly known as Jagaban Gwandu, appeared cheerful and confident while standing among the pilots and cabin crew, reflecting the strong coordination and successful partnership between Kebbi State authorities and the airline handling the pilgrims’ airlift operations.

The atmosphere surrounding the moment was filled with excitement and optimism as the foreign crew members joined local officials in celebrating the smooth commencement of the Hajj transportation exercise.

Observers described the symbolic hand gesture as representing unity, peace, continuity, and confidence in the ongoing developmental strides being witnessed in Kebbi State.

Under the leadership of the Pilgrims Welfare Agency, the state has continued to receive commendation for its organised and efficient handling of Hajj operations, particularly in ensuring the comfort, safety, and welfare of pilgrims from departure to arrival in the Holy Land.

The image has since attracted admiration from supporters and members of the public, many of whom described it as a strong symbol of international cooperation, effective leadership, and the growing reputation of Kebbi State in global religious service operations.

For many supporters, the photograph stands not only as a historic moment during the Hajj airlift exercise, but also as a visual representation of loyalty, continuity, and collective optimism for the future of Kebbi State.

07/05/2026

Babu Shakka Shirye-shiryen wannan Tashar Suna Kara Samun Karbuwa bama Arewa maso Yammacin Najeriya ba Harda Arewa maso Gabashin Najeriya.

Wannan Malamar Tana Bibiyar wannan Tashar Daga Maiduguri.

Muna Godiya Sosai Allah ya kara Bamu ikon Sauke Nauyin Al’umma, na ilmantarwa, Fadakarwa tare da Baku Nishadi.

Address

GRA Rima Roundabout Opposite Ambursa Electronics Birnin Kebbi
Birnin-Kebbi
860101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when I M S Online Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to I M S Online Tv:

Share