14/05/2026
Gwamnatin Jahar Neja tayi Alkawarin Tabbatar da Adalci a Zaben Fidda Gwani na Jam'iyyar APC
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya bai wa dukkan masu neman takara a ƙarƙashin jam’iyyar APC tabbacin gudanar da zaɓen fidda gwani na kai tsaye cikin adalci, gaskiya da kuma nuna cikakken tsari a wuraren da ba a cimma matsayar maslaha ba.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Bologi Ibrahim, ya sanya wa hannu, inda ya ce gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron dabaru da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar tare da dukkan masu neman takara na APC a dakin taro na Hauwa Wali Multipurpose Hall da ke gidan gwamnatin jihar a Minna.
Gwamna Bago ya bayyana cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa da masu neman takara domin samar da maslaha da rage rikice-rikice tare da ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar.
Yayin da ya jaddada cewa jadawalin gudanar da zaɓen fidda gwani bai sauya ba, gwamnan ya bayyana cewa za a gudanar da zaɓen ne a hedikwatar kowace mazaɓa daga cikin mazaɓun jihar baki ɗaya.
Ya kuma gargadi masu neman takara da su guji kawo ’yan daba domin tayar da tarzoma yayin gudanar da zaɓen, yana mai cewa duk wanda aka k**a da hannu wajen hakan na iya fuskantar hukuncin dakatarwa daga takara. Haka kuma ya ce duk wanda ba ɗan jam’iyya ba da aka samu yana kawo cikas za a ɗauki mataki mai tsauri a kansa.
Gwamnan ya yabawa masu neman takarar da s**a janye daga neman muƙami tare da rungumar tsarin maslaha, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da aiki tare da su tare da saka musu da irin sadaukarwar da s**a yi domin ci gaban jam’iyyar.
Har ila yau, ya gode wa jam’iyyar APC bisa nasarar tantance dukkan masu neman takara ba tare da an samu wanda aka dakatar ba, tare da yaba wa duk wadanda s**a halarci taron.
Da yake nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris, ya yabawa Gwamna Bago bisa irin jagorancin da yake bayarwa a cikin jam’iyyar, wanda ya sa da dama daga cikin masu neman takara s**a janye aniyarsu domin samar da haɗin kai.
Ya bayyana cewa wannan wani lokaci ne mai kyau ga jam’iyyar APC da mambobinta, yana mai nuna kwarin gwiwa cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana ba tare da rikici ba, wanda zai zama abin koyi ga sauran jihohin ƙasar nan.
A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Neja, CP Adamu Abdullahi Elleman, ya bukaci masu neman takara da mambobin jam’iyyar da su gudanar da harkokinsu cikin lumana, tare da tabbatar musu da cewa jami’an tsaro za su samar da cikakken tsaro a dukkan mazaɓu 274 na jihar.
CP Elleman ya kuma bukaci dukkan masu neman takara da su je hedikwatar ’yan sanda a ranar Alhamis domin sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya, wadda ya ce tana da muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da zaɓen fidda gwani.
Shugaban APC na shiyyar Arewa ta Tsakiya, Mu’azu Bawa Rijau, da Shugaban APC na jihar, Aminu Musa Bobi, tare da sauran masu ruwa da tsaki da s**a yi jawabi a taron, sun jaddada muhimmancin haɗin kai da gudanar da zaɓen cikin lumana.
Wasu daga cikin masu neman takarar da s**a janye daga takara sun bayyana cewa sun ɗauki matakin ne saboda girmamawa da kuma salon shugabanci na bai wa kowa dama da Gwamna Bago ke nunawa, tare da alƙawarin ci gaba da kasancewa masu biyayya ga jam’iyyar APC.