PEACE TALK TV

PEACE TALK TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from PEACE TALK TV, Camera/Photo, Gusau.
(4)

14/05/2026

Gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da gudanar da zaben fidda gwani kai tsaye, sak**akon matsin lamba daga jiga-jigan 'yan siyasar jihar.

Hukumar EFCC Ta K**a Darakta Janar Na Hukumar Mak**ashi, Mustapha Abdullahi Kan Zargin Wawure Sama Da Naira Biliyan 500J...
13/05/2026

Hukumar EFCC Ta K**a Darakta Janar Na Hukumar Mak**ashi, Mustapha Abdullahi Kan Zargin Wawure Sama Da Naira Biliyan 500

Jami’an Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa na EFCC sun k**a Mustapha Abdullahi, Darakta Janar na Hukumar Mak**ashi ta Najeriya, bisa zargin hannu a laifukan wawure kuɗaɗe da s**a haura Naira biliyan 500.

Rahotanni sun bayyana cewa an k**a shi ne a Abuja a yau Laraba, kuma yanzu haka yana tsare a hannun hukumar domin ci gaba da bincike kan lamarin.

Mai shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya, a ranar Laraba, ya yankewa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mam...
13/05/2026

Mai shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya, a ranar Laraba, ya yankewa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin daurin shekaru 75 a gidan yari bisa laifukan cin hanci da rashawa da s**a shafi ayyukan samar da lantarki na Mambilla da Zungeru.

Alkalin ya same shi da laifi a tuhume-tuhume guda 12, sannan ya bayyana cewa hukuncin zaman gidan yarin zai gudana ne a jere, wanda ya kai jimillar shekaru 75.

Mai shari’a Omotosho ya kuma umarci cewa wa’adin zaman gidan yarin zai fara ne daga ranar da aka k**a Mamman.

Haka kuma, alkalin ya umurci dukkan hukumomin tsaro da su kamo Mamman a duk inda aka same shi.

Kotun ta kuma ba da umarnin a ƙwace dukkan kudade da kadarorin da aka ƙwato daga hannun tsohon ministan domin mayar da su hannun Gwamnatin Tarayya, tare da umartarsa ya mayar da sauran kudaden da s**a rage daga cikin zargin badakalar Naira biliyan 22 da ke da nasaba da ayyukan samar da lantarki na Mambilla da Zungeru.

KOTU A JIYA !Khalifa Sani Zaria ya sanar wa Kotu dukkan abunda ya sani gami da Yunkurin haɗin kai da tuhumar su na kifar...
12/05/2026

KOTU A JIYA !

Khalifa Sani Zaria ya sanar wa Kotu dukkan abunda ya sani gami da Yunkurin haɗin kai da tuhumar su na kifar da Gwamnatin Tinubu.

Khalifa yayiwa Kotu bayanin ne bayan Video Clip da jami'an Gomnaty s**a gabatarwa kotu, khalifa yace tabbas anzo masa da batun juyin mulki cewa Yayi addu'a domin nasara.

Cornell Muhammad Ma'aji shine ya same shi da wannan maganan, amma khalifa ya sanar dasu cewa babu nasara a wannan yunkuri da kuke, domin akwai munafukan da zasu fallasa wannan yunkurin naku. Iya abunda ya sani akai kenan.

Batun kuɗi kuma da aka tura masa yace wannan na Addu'a ne bawai saka hannun sa acikin kifar da gwamnati ba. Sannan yace koda ance me yasa bai sanar da hukuma ga abunda ake shirin aikatawa ba, Yace to wa zai sanarwa, baida alaqa da wani wanda zai iya daukan mataki sannan shi ba ma'aikacin Gomnaty bane.

Yan Zamfara ta Arewa wa kuke fatan ya zama wakilinku a zaben 2027 ?.Ku ajiye muna ra'ayinku a comment section.
12/05/2026

Yan Zamfara ta Arewa wa kuke fatan ya zama wakilinku a zaben 2027 ?.

Ku ajiye muna ra'ayinku a comment section.

Yan Zamfara ta tsakiya wa kuke fatan ya zama wakilinku a zaben 2027 ?.Ku ajiye muna ra'ayinku a comment section.
12/05/2026

Yan Zamfara ta tsakiya wa kuke fatan ya zama wakilinku a zaben 2027 ?.

Ku ajiye muna ra'ayinku a comment section.

Tsohon ɗan majalisar wakilai na Nijeriya, Hon. Abba Anas Adamu, ya rasu a hannun ‘yanbindiga bayan sace shi da s**a yi k...
11/05/2026

Tsohon ɗan majalisar wakilai na Nijeriya, Hon. Abba Anas Adamu, ya rasu a hannun ‘yanbindiga bayan sace shi da s**a yi kan hanyar Kaduna–Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewa a makon da ya gabata ne masu garkuwa da mutane s**a sace wasu manyan ‘yan siyasa daga Jihar Jigawa, ciki har da Abba Anas Adamu, wanda ya taɓa wakiltar mazabar Birniwa/Guri/Kiri Kasama a Majalisar Tarayya kuma ya taɓa shugabantar Karamar Hukumar Guri, tare da Ali Tukur Gantsa, tsohon Sakataren Jam’iyyar PDP na Jihar kuma jigo a Jam’iyyar ADC a jihar, yayin da suke kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Sanata Sabo Mohammed Nakudu (CON) daga Jihar Jigawa ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana ta’aziyyarsa a shafinsa na Facebook.

Rahotanni sun tabbatar cewa Hon. Abba Anas Adamu ya rasu a hannun masu garkuwar, ana kuma sa ran za a kai gawarsa Jihar Jigawa daga yankin Jere da ke Jihar Kaduna a yau Litinin.

A wani bangaren kuma, an samu labarin kubutar Ali Tukur Gantsa daga hannun masu garkuwar.

YANZU - YANZUDaga ɗakin taro na Karma Hotel inda aka kammala dukkan shirye - shirye domin fara tantance ƴan takarar Maja...
11/05/2026

YANZU - YANZU

Daga ɗakin taro na Karma Hotel inda aka kammala dukkan shirye - shirye domin fara tantance ƴan takarar Majalisar dokokin jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin babban kwamitin uwar jam'iyyar APC ta ƙasa da kuma jihar Zamfara.

10/05/2026

Dr Lubna Muhammad Baba Gusau Sarauniyar Kasar Hausa kenan bayan kammala cike form dinta na neman takarar sanata a zamfara central a garin abuja.

Wani harin sojin saman Najeriya ya kashe fararen hula da dama a garin Kasasu na ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar.
10/05/2026

Wani harin sojin saman Najeriya ya kashe fararen hula da dama a garin Kasasu na ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar.

10/05/2026

Wani harin bam wanda aka kai da mota a wani ofishin ‘yansanda a Bannu da ke arewa maso yamacin Pakistan ya kashe ‘yansanda 12 da jikkata aƙalla biyar, k**ar yadda hukumomi s**a sanar.

Address

Gusau

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when PEACE TALK TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category