03/08/2025
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
DARAJOJIN AHLUL BAITI:
Hadisi daga Sayyidah Zainab 'Yar Abu Rafi'in Maulan Manzon Allah (S.A.W) tace :
"Naga Fadimatu (alaihas salam) 'Yar Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) tazo da 'ya'yanta guda biyu wajen Manzon Allah (S.A.W) alokacin da yake jinyarsa wacce aka karbi ransa acikinta.
Sai tace masa "Ya Ma'aikin Allah wadannan 'Ya'yanka ne. To (ina so) ka gadar dasu".
Sai yace "AMMA HASSAN TO NA BASHI KWARJININA DA HALAYEN SHUGABANCINA. AMMA HUSSAINI NA BASHI HALAYEN BAIWA IRIN NAWA DA KUMA JARUMTAKANA".
ADUBA :
- AL-ISABAH Ta Hafiz Ibn Hajr Al'asqalaniy, tarjamah ta 11238.
- USUDUL GHÃBAH NA IBNUL ATHEER (Tarjamah ta 6963).
- TAJREEDU ASMA'IS SAHABAH (Juz'i na 2 shafi na 272).
- IBNU ASAKIRA acikin Tareekh nasa, juzu'i na 4 shafi na 214 da na 414.
- ABU NU'AYM acikin Dala'ilun Nubuwwah.
- KANZUL 'UMMAL na Muntaqal Hindiy hadisi na 34,272. Kuma yace Tabaraniy ma ya ruwaitoshi acikin Mu'ujamul Kabeer da Ibnu Mundah da Ibnu Asakira dukkansu daga Nana Fatimah 'yar Manzon Rahama (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam).
QARIN BAYANI:
Hakika duk wanda ya karanci tarihin wadannan manyan Shugabannin zai tabbatar da cewa tabbas sun gaje halayen Kakansu (S.A.W) fiye da kowanne mahaluki aduniya.
Halayen Shugabanci da jagoranci irin na Imamu Hassan, koda ranar da ya hau kujerar Khalifanci bayan yayi Khutubah sai da ya bama jama'a za'bi. Yace musu "Idan kuna ganin ban chanchanta ba, zan sauka ku zabi duk wanda kuka ga yafi ni dacewa".
Sai s**a ce "Mu mun zabeka Ya 'dan Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam).
Sannan gashi da mutukar kwarjini irin nasu na Ahlul Baiti. Ga yawan murmushi da tawadhu'u da hakuri da juriya, ga kuma zurfin ilimi duk babu k**arsa.
Imamul Husaini shima ya gaje halin baiwa irin na Kakansa domin kuwa alokuta uku daban daban yana kyautar da dukkan abinda ya mallaka baki daya.
Kullum hannayensa cikin kyauta da kyautatawa suke. Bai ta'ba yin rowa ba.
Wajen jarumtaka kuwa,