29/06/2026
Sarki IKon Allah Ran Sarki Yadade
Litini, Muharram 14, 1448AH
Monday, June 29, 2026
DAGA MASARAUTAR ZAZZAU:-
MAI MARTABA SARKIN ZAZZAU YA ZIYARCI IYALAN MARIGAYYA MALAMA UMMULKHAIR A MARARABAN JOS
Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, CFR, da ranan yau bayan dawowarsa daga Babban Birnin Tarayya Abuja, ya jagoranci 'yan Majalisar Masarautar Zazzau wajen gabatar da ta’aziyya ga iyalan Marigayya Malama Ummulkhair wadda fusattatun mutane s**a kashe ba tare da dalili ba a Mararaban Jos.
Wamban Dokon Zazzau, Hakimin Gundumar Rigacikun, Alhaji Ibrahim Sani Zubairu, tare da dagatai da malamai na Gundumar, s**a tarbi Mai Martaba Sarkin Zazzau da isarsa gidan marigayyar.
Mai Martaba Sarkin Zazzau ya nuna bakin ciki da bacin ransa bisa wannan mummunar lamarin, ya kuma gabatar da ta’aziyya ga daukacin iyalan Marigayya Malama Ummulkhair. Ya rokesu da su dauki wannan jarabawa da hakuri da imani da kasancewar kaddara ne daga Allah Madaukaki.
Malam Ahmed Nuhu Bamalli, CFR, ya yi addu’a da fatan: “Allah Ya gafarta wa Malama Ummulkhair kurakurenta, Ya kuma sanya ta cikin Aljannatul Firdaus. Allah Ya ba mijinta, ‘ya’yanta da dukan iyalanta hakuri da daukan juriyyan wannan rashi. Ameen.”_
Mai Martaba Sarkin Zazzau ya jaddada kira ga jama’a da su hakuri su jira sakamakon bincike da matakin da gwamnati za ta dauka, tare da gargadin da su guji daukar doka a hannunsu. Ya ce zaman lafiya, bin tsari da hadin kai ne kawai zai kawo adalci.
- Yaɗa Labarai, na Masarautar Zazzau